Tinubu ya sauke Shugabannin Hukumomi, ma’aikatu da kamfanonin gwamnatin tarayya

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da rushe dukkanin shugabannin hukumomi da ma’aikatu, cibiyoyi da kamfanoni mallakin gwamnatin tarayya, ba tare da bata lokaci ba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya Willie Bassey a daren ranar Litinin a Abuja.

Sanarwar ta ce, hakan yayi dai-dai da karfin ikon da kundin tsarin mulkin kasar ya baiwa shugaban kasa don amfanin jama’a.

‘’Rushewar ba ta shafi kwamitoci da kuma Majalisun da aka jera a Jadawali na Uku, Sashi na 1, Sashi na 153 (i) na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999 da aka yi wa kwaskwarima ba,’’ in ji sanarwar

Dangane da wannan an umarci shugabannin ma’aikatu, Hukumomi, Cibiyoyi, da Kamfanonin Gwamnatin tarayya da su mika ragamar wuraren da suke ga manyan Sakatarorin ma’aikatun domin su cigaba da kula da wuraren.

Ana kuma umurtar manyan sakatarorin su kai irin wadannan wasikun zuwa ga shugaban kasa ta karkashin ofishin sakataren gwamnatin tarayya. Don haka, dukkan Ma’aikatu su tabbatar da bin wannan umarnin da zai fara aiki daga ranar Juma’a 16 ga watan Yuni, 2023.

An umurci manyan sakatarorin da su sanar da shugabannin hukumomin da abin ya shafa a karkashin kulawar ma’aikatu/Ofisoshinsu domin  su bi umarnin cikin gaggawa.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 34 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 59 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com