Home Labarai NLC ta gargaɗi gwamnatin Najeriya kan karin farashin lantarki

NLC ta gargaɗi gwamnatin Najeriya kan karin farashin lantarki

Ƙungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta jingine shirinta na yin ƙarin kuɗin wutar lantarki da kashi 40 cikin 100 cikin wata mai zuwa.

Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Joe Ajaero, ya fitar, ya ce matakin zai ƙara wa ‘yan ƙasar musamman talakawa ”wahalhalu da matsin da suke ciki”.

Kafofin yaɗa labaran Najeriya sun ruwaito hukumar kula da harkokin wutar lantarki ta kasar NERC na shirin ƙara kuɗin wutar daga ranar 1 ga watan Yuli mai zuwa.

A wani mataki na janye tallafin da gwamnatin ƙasar ke biya kan kudin wutar lantarkin.

BBC ta tuntuɓi hukumar ta NERC, don jin bahasinta kan matakin, to amma jami’in hulɗa da jama’a na hukumar Michael Faloseyi ya ce ba a ba shi izinin yin magana kan batun ba.

‘Yan ƙasar da dama sun bayyana kaɗuwarsu kan matakin ƙarin kuɗin wutar lantarkin, suna masu fargabar cewar zai haifar musu da ƙarin matsin tatalin arziki.

A watan da ya gabata ne gwamnatin ƙasar ta sanar da matakin janye tallafin man fetur, lamarin da ya haddasa ƙaruwar farashin man fetur da na kayan abinci a faɗin ƙasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp