Home Labarai Majalisar jihar kano ta Amince a nada kwamishinoni 16 cikin 19

Majalisar jihar kano ta Amince a nada kwamishinoni 16 cikin 19

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da mutane 19 da gwamnan kano ya tura musu don nada su a mukaman kwamishinoni kuma yan majalisar zartarwa ta jiha .

Idan za’a iya tunawa PRNigeria ta rawaito a ranar Talata ne gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf ya aikewa majalisar sunayen mutane 19 da yake so majalisar ta tantance don nada su kwamishinoni.

A ranar jiya Laraba majalisar ta fara aikin tantancewa, yanzu da ta tantance mutane 16 tare da amincewa dasu a Alhamis din nan.

Cikin mutane 19 dai akwai mutum biyu da suka tafi aikin hajji wanda hakan yasa ba a tantance su ba sai kuma mataimakin gwamnan Kano wanda aka amince dashi ba tare da ya halarci tantancewar ba.

Shugaban majalisar Alhaji Isma’il Falgore ya ce sun amincewa gwamnan ya nada mutanen ne, bayan da shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Usaini Dala ya gabatar da kuɗirin hakan, daga bisani bayan tattaunawa akan batun aka amince .

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp