Tinubu ya zarce Landan daga birni Paris

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya kammala ziyarar aiki da ya kai birnin Paris na Faransa, inda kuma zai wuce birnin Landan a yau Asabar, kamar yadda fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

Tun farko an tsara Tinubu zai koma gida Abuja ne bayan kammala taron, wanda shugabannin Afirka suka tattauna harkokin kasuwanci da zuba jari a nahiyar.

“Sai dai yanzu zai wuce birnin Landan na Birtaniya don yin wata ziyara ta ƙashin-kansa,” a cewar sanarwar.

Ta ƙara da cewa shugaban zai koma gida kafin bikin Idin Babbar Sallah, wanda za a fara ranar Laraba.

A ranar Talata Tinubu ya tafi Paris bisa rakiyar wasu daga cikin masu ba shi shawara.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 48 minutes 11 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 29 minutes 36 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com