Kwararru masu binciken kwakwaf sun tabbatar da sahihancin faifen bidiyon da ke nuna tsohon gwamnan jihar Kano Dafta Abdullahi Umar Ganduje na cusa daloli a aljihunsa da aka ce cin hanci ne ya karba daga hannun wasu ‘yan kwangila.
Shugaban Hukumar Sauraren Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin hanci ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana hakan a wani taron yini guda kan yaki da cin hanci da rashawa a jihar.
Ta cikin jawabin nasa Muhyi ya ce, an tabbatar da sahihancin faya-fayan bidiyon.
Read Also:
Inda yace tun lokacin da aka saki hotunan bidiyon, jama’a ke ta kalubalantar hukumar da ta wanke gwamnan daga wannan zargi ko kuma akasin haka.
A shekarar 2017, Jaridar Daily Nigerian da ake wallafawa a yanar gizo ta saki wasu hotunan bidiyon Ganduje na karbar kudadden da ake zargin cewa, na cin hanci ne, al’amarin da ya haddasa cece-kuce a ciki da wajen jihar.
Muhyi ya ce, tun a shekarar 2018 ne suka kaddamar da bincike kan lamarin, amma suka gaza zurfafa binciken Gandujen saboda a lokacin saboda rigar kariya da yake da ita a matsayinsa na gwamna.
PRNigeria hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 18 hours 34 minutes 58 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 16 minutes 23 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com