Majalisar wakilai ta dakatar da JAMB daga hukunta yarinyar da ‘ta ƙara wa kanta maki’

Majalisar wakilai ta Najeriya ta tsoma baki cikin batun zargin da hukumar shirya jarabawar shiga jami’a (JAMB) ta yi wa wata daliba mai suna Mmesoma Ejikeme na kirkirar sakamakon jarabawa na bogi wanda hukumar ta shirya na shekarar 2023.

‘Yan majalisar sun nuna damuwarsu kan yadda hukumar jarabawar ta gaza nuna dattaku kan lamarin da ya shafi karamar yarinya ta hanyar janye sakamakon jarabawarta tare da dakatar da ita na tsawon shekaru uku.

Sun ce yana yiwuwa akwai hannun wani a cikin lamarin.

Daga nan ne majalisar ta kafa kwamitin da zai binciki lamarin tare da neman hukumar JAMB da ta dakatar da zartar da hukunci har sai majalisar ta kammala bincikenta.

A ranar Lahadin da ta gabata ne hukumar ta JAMB ta zargi dalibar da kirkirar sakamakon bogi a jarabawar ta bana.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 12 hours 1 minute 59 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 43 minutes 24 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com