Home Labarai Jirgin hirar da Sojin Nijeriya yayi Hadari a Makurdi

Jirgin hirar da Sojin Nijeriya yayi Hadari a Makurdi

Wani jirgin saman horar da sojojin saman Najeriya FT-7NI ya yi hatsari a Makurdi, babban birnin jihar Benue.

Bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a, yayin da ake wani aikin horo.

Daraktan hulda da jama’a da yaɗa labarai na rundunar sojin sama ta Najeriya, Air Commodore Edward Gabkwet ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Ya ce matukan jirgi biyu na samun kulawa a asibitin sojojin sama da ke brinin Makurdi.

“An yi sa’a, matukan jirgin biyu da ke cikin jirgin sun tsira daga hatsarin bayan da suka yi nasarar ficewa daga cikin jirgin. Bugu da kari, babu asarar rayuka ko asarar dukiya a inda hatsarin ya faru.

Ya ƙara da cewa a halin da ake ciki, babban hafsan sojin sama na Najeriya, Air Vice Marshal Hassan Abubakar, ya kafa kwamitin bincike domin gano musabbabin hatsarin nan take.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp