Home Labarai Gwamnatin Jihar Kano zata samar da doka don masu zubar da Shara

Gwamnatin Jihar Kano zata samar da doka don masu zubar da Shara

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa baza ta lamunci zubar da Shara da wasu Al’ummar jihar ke yi ba bisa ka’ida ba.

Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Ambassador Alhaji Ahmadu Haruna Zago ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai a zagayen gani da ido da yake yi kan yadda aikin kwashe Shara ke cigaba da gudana a wasu sassan jihar.

Dan Zago ya kuma tabbatar da cewa nan gaba kadan gwamnati zata Samar da tsarin da zai Kara jaddada dokar hana zubar da shara barkatai musamman a wuraren da Al’umma ke sake jibgewa sharar bayan gwamnati ta kwashe.

Yace, la’akari da yadda wasu daga cikin al’ummomin da aka kwashe sharar su a kwanakin baya suka sake jibge sharar a wuraren, hakan na nufin dole sai gwamnati ta fito da tsarin da zai karfafa dokar zubar da shara ga al’umma musamman a wuraren da aka tanada domin zubarwa.

Suma wasu daga cikin al’ummomin da aka kwashe sharar dake yankunansu musamman na kan titin Katsina daura da makabartar abbatuwa sun bayyana irin cikakken hadin kan da zasu baiwa gwamnati domin tsaftace Muhallansu da titunansu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp