Home Labarai Babbar Kotun tarayya ta dakatar da yunkurin gayyatar tsohon Gwamna Ganduje

Babbar Kotun tarayya ta dakatar da yunkurin gayyatar tsohon Gwamna Ganduje

Babbar kotun tarayya dake zamanta a jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a A M Liman ta dakatar da hukumar karbar korafe korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar da sauran hukumomin tsaro daga gayyata ko kama tsohon Gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Wannan na kunshe ne cikin wata dakatarwa ta wucin gadi da kotun tayi har sai ta saurari karar dake gabanta data shafi zargin take hakkin Dan Adam da tsohon Gwamna Ganduje ya shigar.

Kotun dai ta sanya ranar 14 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata fara sauraron karar.

Hukumar ta PCACC dai ta aikawa tsohon Gwamnan da takardar gayyata domin amsa tambayoyi kan wani fefan Bidiyo da ake zargin Ganduje na karbar kudaden kasashen waje, duk kuwa da cewa yasha musantawa.

A ranar alhamis data gabata, bayan bullar waccen gayyata, Jam’iyyar APC mai hamayya a Kano ta fitar da wata sanarwa inda take kira ga tsohon Gwamnan da yayi watsi da waccen gayyata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp