Babbar kotun tarayya dake zamanta a jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a A M Liman ta dakatar da hukumar karbar korafe korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar da sauran hukumomin tsaro daga gayyata ko kama tsohon Gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.
Wannan na kunshe ne cikin wata dakatarwa ta wucin gadi da kotun tayi har sai ta saurari karar dake gabanta data shafi zargin take hakkin Dan Adam da tsohon Gwamna Ganduje ya shigar.
Read Also:
Kotun dai ta sanya ranar 14 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata fara sauraron karar.
Hukumar ta PCACC dai ta aikawa tsohon Gwamnan da takardar gayyata domin amsa tambayoyi kan wani fefan Bidiyo da ake zargin Ganduje na karbar kudaden kasashen waje, duk kuwa da cewa yasha musantawa.
A ranar alhamis data gabata, bayan bullar waccen gayyata, Jam’iyyar APC mai hamayya a Kano ta fitar da wata sanarwa inda take kira ga tsohon Gwamnan da yayi watsi da waccen gayyata.











