Home Labarai Babbar Kotun tarayya ta dakatar da yunkurin gayyatar tsohon Gwamna Ganduje

Babbar Kotun tarayya ta dakatar da yunkurin gayyatar tsohon Gwamna Ganduje

Babbar kotun tarayya dake zamanta a jihar Kano karkashin jagorancin mai shari’a A M Liman ta dakatar da hukumar karbar korafe korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar da sauran hukumomin tsaro daga gayyata ko kama tsohon Gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Wannan na kunshe ne cikin wata dakatarwa ta wucin gadi da kotun tayi har sai ta saurari karar dake gabanta data shafi zargin take hakkin Dan Adam da tsohon Gwamna Ganduje ya shigar.

Kotun dai ta sanya ranar 14 ga watan Yuli a matsayin ranar da zata fara sauraron karar.

Hukumar ta PCACC dai ta aikawa tsohon Gwamnan da takardar gayyata domin amsa tambayoyi kan wani fefan Bidiyo da ake zargin Ganduje na karbar kudaden kasashen waje, duk kuwa da cewa yasha musantawa.

A ranar alhamis data gabata, bayan bullar waccen gayyata, Jam’iyyar APC mai hamayya a Kano ta fitar da wata sanarwa inda take kira ga tsohon Gwamnan da yayi watsi da waccen gayyata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp