Home Labarai INEC ta shigar da karar Hudu Ari gaban kotu

INEC ta shigar da karar Hudu Ari gaban kotu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) ta shigar da tuhume-tuhume shida a gaban kotu, kan dakataccen kwamishinan zabe na jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar mai dauke da sannun shugaban sashen wayar da kan al’umma na hukumar, Festus Okoye, ta ce an shigar da ƙarar ce a babbar kotun jiha da ke Yola, a jihar Adamawa.

Sanarwar ta kuma tabbatar da samun takardar kammala bincike kan laifukan da suka shafi zabe daga hannun ‘yan sanda, bayan kammala bincike kan laifukan zabe da aka yi a babban zaben na 2023, ciki har da wanda ya shafi Ari.

Sanarwar ta ce, “Kamar yadda sashe na 145 (1) na dokar zabe ta 2022 ya tanadar, laifin da aka aikata a ƙarƙashin dokar za a iya gurfanar da shi a gaban kotun majistare ko kuma babbar kotun jihar da aka aikata laifin, ko kuma babban birnin tarayya, Abuja.

Bayanin ya ƙara da cewa Kotu ta sanya ranar Laraba 12 ga Yulin 2023 don fara shari’ar.

Yunusa-Ari dai ya shiga matsala ne bayan kammala zaben gwamnan jihar Adamawa a ranar 15 ga Afrilun 2023, lokacin da ya bayyana Aisha Dahiru ‘Binani’ ta jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaben da aka gudanar a yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp