‘Yan bindiga sun hallaka mutum daya a jihar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina dake arewa maso yammacin Nijeiya ta tabbatar ta mutuwar mutum daya sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kankia ta jihar.

kakakin hukmar ƴan sandan jihar, ASP Abubakar Aliyu, ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tuni ƴan sanda suka fara bincike kan lamarin domin kamo waɗanda ke da hannu a kai harin.

‘yan bindigan sun harbi mutumin ne lokacin da suka kai hari wani rukunin gidaje da ke unguwar low-cost kusa da babban asibitin karamar hukumar a daren Asabar.

Wani ganau ya bayyana cewa ƴan bindigar sun zo ne a kan babura, inda suka yi wa rukunin gidajen dirar miƙiya tare da harbi kan mai uwa da wabi, abin da kuma ya janyo mutuwar mutumin mai suna Alhaji Ibrahim Baraya Solo.

Bayan kashe mutumin ne, sai maharan suka tsere tare da barinsa cikin jini.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 29 minutes 35 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 11 minutes 0 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com