Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Matar shugaban Nijeriya Uwargida Oluremi Tinubu ta karbi Rebecca Kabu guda cikin daliban Makarantar Chibok 277 da mayakan Boko Haram suka sace a shekarar 2014.

Oluremi ta karbi dalibar ne a fadar shugaban kasa dake Villa tare da matar mataimakin shugaban kasar , Hajia Nana Shettima, inda tayi alkawarin lura da lafiya ta tare da daukar nauyin karatunta.

Ta kuma tabbatar da cewa ba a manta da sauran daliban da ke tsare a hannun ‘yan ta’addan ba.

Haka Kuma ta yaba da kokarin ofishin babban mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran jami’an tsaro bisa kokarin su na kubutar da Rebbeca.

An dai sace daliban na makarantar Chibok ne a wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram suka kai kan daliban Makarantar ta Chibok dake Jihar Borno a Arewa maso ga bashin Nijeriya tun a shekarar 2014.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 27 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 9 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com