Home Labarai Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Matar shugaban Nijeriya Uwargida Oluremi Tinubu ta karbi Rebecca Kabu guda cikin daliban Makarantar Chibok 277 da mayakan Boko Haram suka sace a shekarar 2014.

Oluremi ta karbi dalibar ne a fadar shugaban kasa dake Villa tare da matar mataimakin shugaban kasar , Hajia Nana Shettima, inda tayi alkawarin lura da lafiya ta tare da daukar nauyin karatunta.

Ta kuma tabbatar da cewa ba a manta da sauran daliban da ke tsare a hannun ‘yan ta’addan ba.

Haka Kuma ta yaba da kokarin ofishin babban mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran jami’an tsaro bisa kokarin su na kubutar da Rebbeca.

An dai sace daliban na makarantar Chibok ne a wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram suka kai kan daliban Makarantar ta Chibok dake Jihar Borno a Arewa maso ga bashin Nijeriya tun a shekarar 2014.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp