Home General Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Shalkwatar tsaron kasa ta yi watsi da masu kira kan sojojinta da su yi katsalandan a tsarin dimokradiyyar kasar nan.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Asabar, in da tace sojojin kasar sun nuna rashin jin dadinsu kan wani labari da ake yadawa a yanar gizo kan cewa akwai wasu matsaloli game da batun jin dadi da walwalwa na sojojin kasar.

Sanarwar ta ce shugaban sojin kasar Janar CG Musa ya kara jaddada biyayyarsa ga Shugaba Tinubu inda ya ce ba zai kauce wa aikinsa da kundin tsarin mulkin kasar na 1999 ya tsara ba.

“Kiraye-kirayen da ake yi kan sojoji da su yi katsalandan a dimokradiyya rashin kishin kasa ne, da mugunta da kuma yunkurin kawar da hankalin sojojin Nijeriya daga gudanar da ayyukansu da kundin tsarin mulki ya tsara,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

“Ganin cewa rundunar sojin Nijeriya tana mayar da hankali wurin kyautata wa dakarunta, ba ma son duk wani yunkuri na wani ko wata kungiya da za ta harzuka Sojojin Nijeriya masu bin doka domin su tunkari sauyin gwamnati wanda kundin tsarin mulkin kasar bai amince da shi ba.

“Muna so mu bayyana cewa ba shakka sojoji suna farin ciki kuma sun fi dacewa a karkashin mulkin dimokradiyya kuma ba za su shiga duk wani aiki na zagon kasa ga dimokradiyyar da aka samu a kasarmu ba,” in ji sanarwar.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen dake Nahiyar Afirka ke fuskantar katsalandan da sojojin ke yi a harkokin Damukradiyya abin da wasu ke kallon shine Mafita ga nahiyar, in da nasan harkokin yau da kullum da cigaban Al’umma ke Allawadai da katsalandan din kasancewar shike sake mayar da nahiyar ta Afrika baya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp