Home General Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Shalkwatar tsaron kasa ta yi watsi da masu kira kan sojojinta da su yi katsalandan a tsarin dimokradiyyar kasar nan.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Asabar, in da tace sojojin kasar sun nuna rashin jin dadinsu kan wani labari da ake yadawa a yanar gizo kan cewa akwai wasu matsaloli game da batun jin dadi da walwalwa na sojojin kasar.

Sanarwar ta ce shugaban sojin kasar Janar CG Musa ya kara jaddada biyayyarsa ga Shugaba Tinubu inda ya ce ba zai kauce wa aikinsa da kundin tsarin mulkin kasar na 1999 ya tsara ba.

“Kiraye-kirayen da ake yi kan sojoji da su yi katsalandan a dimokradiyya rashin kishin kasa ne, da mugunta da kuma yunkurin kawar da hankalin sojojin Nijeriya daga gudanar da ayyukansu da kundin tsarin mulki ya tsara,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

“Ganin cewa rundunar sojin Nijeriya tana mayar da hankali wurin kyautata wa dakarunta, ba ma son duk wani yunkuri na wani ko wata kungiya da za ta harzuka Sojojin Nijeriya masu bin doka domin su tunkari sauyin gwamnati wanda kundin tsarin mulkin kasar bai amince da shi ba.

“Muna so mu bayyana cewa ba shakka sojoji suna farin ciki kuma sun fi dacewa a karkashin mulkin dimokradiyya kuma ba za su shiga duk wani aiki na zagon kasa ga dimokradiyyar da aka samu a kasarmu ba,” in ji sanarwar.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen dake Nahiyar Afirka ke fuskantar katsalandan da sojojin ke yi a harkokin Damukradiyya abin da wasu ke kallon shine Mafita ga nahiyar, in da nasan harkokin yau da kullum da cigaban Al’umma ke Allawadai da katsalandan din kasancewar shike sake mayar da nahiyar ta Afrika baya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp