Home Labarai Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Matar shugaban Nijeriya Uwargida Oluremi Tinubu ta karbi Rebecca Kabu guda cikin daliban Makarantar Chibok 277 da mayakan Boko Haram suka sace a shekarar 2014.

Oluremi ta karbi dalibar ne a fadar shugaban kasa dake Villa tare da matar mataimakin shugaban kasar , Hajia Nana Shettima, inda tayi alkawarin lura da lafiya ta tare da daukar nauyin karatunta.

Ta kuma tabbatar da cewa ba a manta da sauran daliban da ke tsare a hannun ‘yan ta’addan ba.

Haka Kuma ta yaba da kokarin ofishin babban mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran jami’an tsaro bisa kokarin su na kubutar da Rebbeca.

An dai sace daliban na makarantar Chibok ne a wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram suka kai kan daliban Makarantar ta Chibok dake Jihar Borno a Arewa maso ga bashin Nijeriya tun a shekarar 2014.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp