Home Labarai Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Guda cikin daliban Chibok ta kubuta

Matar shugaban Nijeriya Uwargida Oluremi Tinubu ta karbi Rebecca Kabu guda cikin daliban Makarantar Chibok 277 da mayakan Boko Haram suka sace a shekarar 2014.

Oluremi ta karbi dalibar ne a fadar shugaban kasa dake Villa tare da matar mataimakin shugaban kasar , Hajia Nana Shettima, inda tayi alkawarin lura da lafiya ta tare da daukar nauyin karatunta.

Ta kuma tabbatar da cewa ba a manta da sauran daliban da ke tsare a hannun ‘yan ta’addan ba.

Haka Kuma ta yaba da kokarin ofishin babban mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran jami’an tsaro bisa kokarin su na kubutar da Rebbeca.

An dai sace daliban na makarantar Chibok ne a wani hari da mayakan kungiyar Boko Haram suka kai kan daliban Makarantar ta Chibok dake Jihar Borno a Arewa maso ga bashin Nijeriya tun a shekarar 2014.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp