Home General Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Sojojin Nijeriya basu da shirin juyin Mulki – HDQ

Shalkwatar tsaron kasa ta yi watsi da masu kira kan sojojinta da su yi katsalandan a tsarin dimokradiyyar kasar nan.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Asabar, in da tace sojojin kasar sun nuna rashin jin dadinsu kan wani labari da ake yadawa a yanar gizo kan cewa akwai wasu matsaloli game da batun jin dadi da walwalwa na sojojin kasar.

Sanarwar ta ce shugaban sojin kasar Janar CG Musa ya kara jaddada biyayyarsa ga Shugaba Tinubu inda ya ce ba zai kauce wa aikinsa da kundin tsarin mulkin kasar na 1999 ya tsara ba.

“Kiraye-kirayen da ake yi kan sojoji da su yi katsalandan a dimokradiyya rashin kishin kasa ne, da mugunta da kuma yunkurin kawar da hankalin sojojin Nijeriya daga gudanar da ayyukansu da kundin tsarin mulki ya tsara,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

“Ganin cewa rundunar sojin Nijeriya tana mayar da hankali wurin kyautata wa dakarunta, ba ma son duk wani yunkuri na wani ko wata kungiya da za ta harzuka Sojojin Nijeriya masu bin doka domin su tunkari sauyin gwamnati wanda kundin tsarin mulkin kasar bai amince da shi ba.

“Muna so mu bayyana cewa ba shakka sojoji suna farin ciki kuma sun fi dacewa a karkashin mulkin dimokradiyya kuma ba za su shiga duk wani aiki na zagon kasa ga dimokradiyyar da aka samu a kasarmu ba,” in ji sanarwar.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasashen dake Nahiyar Afirka ke fuskantar katsalandan da sojojin ke yi a harkokin Damukradiyya abin da wasu ke kallon shine Mafita ga nahiyar, in da nasan harkokin yau da kullum da cigaban Al’umma ke Allawadai da katsalandan din kasancewar shike sake mayar da nahiyar ta Afrika baya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp