Home Labarai Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Dakarun haɗin gwiwar sojojin Najeriya da na jami’an DSS sun ce sun yi nasarar daƙile wani hari da wasu ‘yan tayar da ƙayar bayan Boko Haram suka shirya kai wa a Kano da ke arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta wallafa a shafinta an X ta ce, hadin gwiwar jami’an tsaron sun kai wani ƙaramar hukumar Gezawa da ke jihar Kano, da nufin ganowa tare da kama wasu da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne da ake kyautata zaton suna shirin wani gagarumin farmaki a Kano.

Sanarwar ta ce a lokacin samamen, jami’an tsaron sun kama mutum biyu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, kuma an ƙwato manyan makamai da ababen fashewa.

“Wannan farmakin ya nuna kyakkyawan hadin gwiwa da ke tsakanin jami’an tsaron da kuma jajircewar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro na dakile ta’addanci da kuma inganta tsaro a faɗin ƙasar”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar Sojin ƙasar ta ƙarfafa wa jama’a gwiwa don bayar da muhimman bayanan da za su taimaka wa ƙoƙarin suke yi yi na magance matsalar tsaro a ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp