Home Labarai Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi...

Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi ba

Mai shari’a Adegbola Adeniyi na babbar kotun birnin tarayya, ya bayar da umarnin a gaggauta sakin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele ba tare da wani sharaɗi ba.

Wannan umarni ya zo ne a matsayin martani ga wata buƙatar gaggawa da Emefiele ya shigar, inda ya buƙaci a sake shi daga hannun Hukumar Yaƙi da cin Hanci da Rashawa Ta Najeriya (EFCC).

Kotun ta umurci hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu a ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, 2023, wadda ita ce ranar da aka sanya da za a ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar, tare da yiwuwar kotu ta bayar da belinsa.

Emefiele dai ya shigar da buƙatar gaggawar ne a gaban kotu, inda ya buƙaci a tilasta wa hukumar EFCC ta sake shi daga gidan yari, har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan shari’ar da ya dace.

A ranar 9 ga watan Yuni ne dai shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele daga mukaminsa na shugaban babban bankin ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp