Home Labarai Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi...

Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi ba

Mai shari’a Adegbola Adeniyi na babbar kotun birnin tarayya, ya bayar da umarnin a gaggauta sakin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele ba tare da wani sharaɗi ba.

Wannan umarni ya zo ne a matsayin martani ga wata buƙatar gaggawa da Emefiele ya shigar, inda ya buƙaci a sake shi daga hannun Hukumar Yaƙi da cin Hanci da Rashawa Ta Najeriya (EFCC).

Kotun ta umurci hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu a ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, 2023, wadda ita ce ranar da aka sanya da za a ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar, tare da yiwuwar kotu ta bayar da belinsa.

Emefiele dai ya shigar da buƙatar gaggawar ne a gaban kotu, inda ya buƙaci a tilasta wa hukumar EFCC ta sake shi daga gidan yari, har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan shari’ar da ya dace.

A ranar 9 ga watan Yuni ne dai shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele daga mukaminsa na shugaban babban bankin ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp