Home Labarai Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi...

Kotu ta umarci EFCC ta saki Emefiele ba tare da wani shardi ba

Mai shari’a Adegbola Adeniyi na babbar kotun birnin tarayya, ya bayar da umarnin a gaggauta sakin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele ba tare da wani sharaɗi ba.

Wannan umarni ya zo ne a matsayin martani ga wata buƙatar gaggawa da Emefiele ya shigar, inda ya buƙaci a sake shi daga hannun Hukumar Yaƙi da cin Hanci da Rashawa Ta Najeriya (EFCC).

Kotun ta umurci hukumar EFCC ta gurfanar da Emefiele a gaban kotu a ranar Litinin 6 ga watan Nuwamba, 2023, wadda ita ce ranar da aka sanya da za a ci gaba da sauraron ƙarar da aka shigar, tare da yiwuwar kotu ta bayar da belinsa.

Emefiele dai ya shigar da buƙatar gaggawar ne a gaban kotu, inda ya buƙaci a tilasta wa hukumar EFCC ta sake shi daga gidan yari, har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan shari’ar da ya dace.

A ranar 9 ga watan Yuni ne dai shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele daga mukaminsa na shugaban babban bankin ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp