Home Labarai Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Dakarun haɗin gwiwar sojojin Najeriya da na jami’an DSS sun ce sun yi nasarar daƙile wani hari da wasu ‘yan tayar da ƙayar bayan Boko Haram suka shirya kai wa a Kano da ke arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta wallafa a shafinta an X ta ce, hadin gwiwar jami’an tsaron sun kai wani ƙaramar hukumar Gezawa da ke jihar Kano, da nufin ganowa tare da kama wasu da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne da ake kyautata zaton suna shirin wani gagarumin farmaki a Kano.

Sanarwar ta ce a lokacin samamen, jami’an tsaron sun kama mutum biyu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, kuma an ƙwato manyan makamai da ababen fashewa.

“Wannan farmakin ya nuna kyakkyawan hadin gwiwa da ke tsakanin jami’an tsaron da kuma jajircewar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro na dakile ta’addanci da kuma inganta tsaro a faɗin ƙasar”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar Sojin ƙasar ta ƙarfafa wa jama’a gwiwa don bayar da muhimman bayanan da za su taimaka wa ƙoƙarin suke yi yi na magance matsalar tsaro a ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp