Home Labarai Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Jami’an tsaron sun kama ‘yan boko haram a Kano

Dakarun haɗin gwiwar sojojin Najeriya da na jami’an DSS sun ce sun yi nasarar daƙile wani hari da wasu ‘yan tayar da ƙayar bayan Boko Haram suka shirya kai wa a Kano da ke arewacin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta wallafa a shafinta an X ta ce, hadin gwiwar jami’an tsaron sun kai wani ƙaramar hukumar Gezawa da ke jihar Kano, da nufin ganowa tare da kama wasu da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne da ake kyautata zaton suna shirin wani gagarumin farmaki a Kano.

Sanarwar ta ce a lokacin samamen, jami’an tsaron sun kama mutum biyu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne, kuma an ƙwato manyan makamai da ababen fashewa.

“Wannan farmakin ya nuna kyakkyawan hadin gwiwa da ke tsakanin jami’an tsaron da kuma jajircewar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro na dakile ta’addanci da kuma inganta tsaro a faɗin ƙasar”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar Sojin ƙasar ta ƙarfafa wa jama’a gwiwa don bayar da muhimman bayanan da za su taimaka wa ƙoƙarin suke yi yi na magance matsalar tsaro a ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp