Home Labarai Tinubu ya Amince da nadin mai bashi shawara kan masu bukata ta...

Tinubu ya Amince da nadin mai bashi shawara kan masu bukata ta musamman

Shugaban ƙasar Nigeria Bola Tinubu ya amince da nadin Muhammad Abba Isa a matsayin babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin masu bukata ta musamman.

A cewar wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Alhamis, yace nadin na cikin kudirin Tinubu na tabbatar da cewa kowane bangare na al’umma ya samu isasshiyar dama a gwamnatin sa.

“Muhammad Abba Isa fitacce ne wanda ya kwashe sama da shekaru 10 yana bada shawarwarin yadda za’a inganta rayuwar Masu bukaci ta musamman a gida Nigeria da kasashen waje,” in ji sanarwar.

“Sabon mai taimaka wa shugaban kasa ya kammala karatunsa kan harkokin mulki a jami’ar Maiduguri, inda kuma yayi Digirin na biyu a wannan fannin a dai jami’ar ta Maiduguri a shekarar 2017.

Shugaban ya bukaci sabon mai bashi shawara da ya samar da hanyoyin da za a bi don shigar da masu bukata ta musamman cikin manufofi da shirye-shiryen dukkan ma’aikatu, sassan da hukumomin gwamnatin tarayya tare da yin aiki kafada da kafada da kananan hukumomi don aiwatar da shirin, don inganta rayuwar su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp