Home Labarai An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

Masu garkuwa da mutane sun saki ɗaliba ɗaya daga cikin biyar da aka sace daga jami’ar tarayya ta Dutsen-ma da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan ɗaliban sun kwashe kwana 45 a hannun ƴan bindigar.

Shugaban jami’ar ya tabbatar da kubutar ɗaya daga cikin ɗaliban, sai dai bai fayyace ko an biya kuɗi ba kafin sakin nata.

A ranar 4 ga watan Oktoba ne wasu ƴan fashi suka kutsa ɗakunan kwanan ɗaliban tare da yin awon-gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan sace wasu ɗalibai a Jami’ar Tarayya ta Gusau.

Satar mutane domin neman kuɗin fansa wata matsala ce da ta addabi yankin arewacin Najeriya, inda ƴan fashi kan far wa al’umma a ƙauyuka da makarantu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp