Home Labarai Obasanjo ya kalubalnaci hukuncin kotu kan zaben Gwamnoni

Obasanjo ya kalubalnaci hukuncin kotu kan zaben Gwamnoni

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya caccaki hukuncin da alƙalan Najeriya suka yanke kan shari’o’in zaɓe, yana mai cewa bai kamata alƙalai uku zuwa biyar su soke hukuncin da miliyoyin masu kada ƙuri’a suka yanke a lokacin zabe ba.

Obasanjo ya bayyana ikon da wasu alƙalai ƙalilan ke da shi a matsayin al’amari da “ba za a amince da shi ba.”

Tsohon shugaban ƙasar ya yi magana ne dangane da hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ke ci gaba da yi kan taƙaddamar zaɓe ta bayan zaɓen 2023 a Najeriya.

A makon da ya gabata ne dai wasu alƙalan kotun ɗaukaka ƙara suka yanke hukuncin korar wasu gwamnoni uku daga aiki.

Lokacin da yake tsokaci a wani taro sake fasalin dimokuraɗiyya domin amfanin ƙasashen Afirka, a garin Abeokuta na jihar Ogun, ya ce tsarin mulkin dimokuraɗiyya na ƙasashen yamma ba zai taɓa yin daidai da ƙasashen Afirka ba kasancewar ba ya la’akari da ra’ayin mafi yawan al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp