Masu garkuwa da mutane sun saki ɗaliba ɗaya daga cikin biyar da aka sace daga jami’ar tarayya ta Dutsen-ma da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.
Hakan na zuwa ne bayan ɗaliban sun kwashe kwana 45 a hannun ƴan bindigar.
Shugaban jami’ar ya tabbatar da kubutar ɗaya daga cikin ɗaliban, sai dai bai fayyace ko an biya kuɗi ba kafin sakin nata.
Read Also:
A ranar 4 ga watan Oktoba ne wasu ƴan fashi suka kutsa ɗakunan kwanan ɗaliban tare da yin awon-gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.
Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan sace wasu ɗalibai a Jami’ar Tarayya ta Gusau.
Satar mutane domin neman kuɗin fansa wata matsala ce da ta addabi yankin arewacin Najeriya, inda ƴan fashi kan far wa al’umma a ƙauyuka da makarantu.
PRNigeria Hausa
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 20 hours 55 minutes 9 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 36 minutes 34 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com