Home Labarai An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

Masu garkuwa da mutane sun saki ɗaliba ɗaya daga cikin biyar da aka sace daga jami’ar tarayya ta Dutsen-ma da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan ɗaliban sun kwashe kwana 45 a hannun ƴan bindigar.

Shugaban jami’ar ya tabbatar da kubutar ɗaya daga cikin ɗaliban, sai dai bai fayyace ko an biya kuɗi ba kafin sakin nata.

A ranar 4 ga watan Oktoba ne wasu ƴan fashi suka kutsa ɗakunan kwanan ɗaliban tare da yin awon-gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan sace wasu ɗalibai a Jami’ar Tarayya ta Gusau.

Satar mutane domin neman kuɗin fansa wata matsala ce da ta addabi yankin arewacin Najeriya, inda ƴan fashi kan far wa al’umma a ƙauyuka da makarantu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp