Home Labarai An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

An saki ɗaliba ɗaya cikin biyar da aka sace a jami’ar Dutsin-Ma

Masu garkuwa da mutane sun saki ɗaliba ɗaya daga cikin biyar da aka sace daga jami’ar tarayya ta Dutsen-ma da ke jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan ɗaliban sun kwashe kwana 45 a hannun ƴan bindigar.

Shugaban jami’ar ya tabbatar da kubutar ɗaya daga cikin ɗaliban, sai dai bai fayyace ko an biya kuɗi ba kafin sakin nata.

A ranar 4 ga watan Oktoba ne wasu ƴan fashi suka kutsa ɗakunan kwanan ɗaliban tare da yin awon-gaba da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Hakan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan sace wasu ɗalibai a Jami’ar Tarayya ta Gusau.

Satar mutane domin neman kuɗin fansa wata matsala ce da ta addabi yankin arewacin Najeriya, inda ƴan fashi kan far wa al’umma a ƙauyuka da makarantu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp