‘yan bindiga sun hallaka Mutane 4 a jihar Katsina

Taswirar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina ta tabbatar da mutuwar mutane hudu, inda takwas suka bata sakamakon harin ‘yan bindiga a wasu garuruwan jihar.

kakakin rundunar ASP Abubakar Aliyu ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce ‘yan bindigar sun aukawa wasu manoma a kayukan Dantsuntu da Nahuta a karamar hukumar batsari, in da suka hallaka mutane 4.

yayin da yake ganawa da manema labarai ASP ALiyu yace tuni rundunar ‘yan sanda ta sami labarin aukuwar lamari, haka kuma ya tabbatar da batan mutane 4 sakamakon harin ‘yan ta’addan.

wani daga cikin wadanda suka kubuta daga harin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa ya ce harin na daga cikin hare haren da ‘yan bindigar suke kaiwa kauyuka, wanda hakan ke haifar musu da shiga mawuyacin hali wajen gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum, wanda hakan baya barin su zuwa gonakin su.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 29 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 11 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com