Home Labarai DHQ ta tabbatar da labarin PRNigeria na hallaka, Ali Kachalla

DHQ ta tabbatar da labarin PRNigeria na hallaka, Ali Kachalla

Maj.-Gen. Edward Buba, Director, Defence Media Operations, and Brigadier General Tukur Ismaila Gusau, Defence Spokesperson

Shalkwatar rundunar sojojin Nijeriya ta tattabar da labarin da PRNigeria ta wallafa na hallaka jagoran ‘yan bindiga Ali Kachalla bisa wani harin jirgin sama da rundunar sojin saman Kasar ta kai sansanin su.

wata majiya daga rundunar ta tabbatarwa da PRNigeria cewa  ta cikin wani harin da sojojin saman suka kai sun sami nasarar hallaka ‘yan ta’adda hudu cikin su kuwa harda Ali Kachalla.

daraktan yada labaran shalkwatar, Manjo Janar Edward Buba, ya bayyana cewa sauran wadanda suka gamu da ajalin nasu sun hadar da Machika, Haro da Dan Muhammadu.

idan dai zaku iya tunawa a ranar 11 ga watan Disambar PRNigeria ta wallafa labarin dake cewa wani harin sojojin saman Nijeriya ya hallaka Ali Kachalla bayan wani yunkurin kai hari da shi da tawagar su suka kitsa kan dakarun sojojin dake sintiri a jihar Niger.

PRNigeria ta tattara bayanai daga majiyar tsaron ta cewa Ali kacchalla ya gamu da ajalin sa sakamakon wani hari da dakarun da aka girke a garin Mangoro na karamar hukumar Munya ta jihar Niger.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp