Home Labarai ‘yan bindiga sun hallaka Mutane 4 a jihar Katsina

‘yan bindiga sun hallaka Mutane 4 a jihar Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina ta tabbatar da mutuwar mutane hudu, inda takwas suka bata sakamakon harin ‘yan bindiga a wasu garuruwan jihar.

kakakin rundunar ASP Abubakar Aliyu ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce ‘yan bindigar sun aukawa wasu manoma a kayukan Dantsuntu da Nahuta a karamar hukumar batsari, in da suka hallaka mutane 4.

yayin da yake ganawa da manema labarai ASP ALiyu yace tuni rundunar ‘yan sanda ta sami labarin aukuwar lamari, haka kuma ya tabbatar da batan mutane 4 sakamakon harin ‘yan ta’addan.

wani daga cikin wadanda suka kubuta daga harin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa ya ce harin na daga cikin hare haren da ‘yan bindigar suke kaiwa kauyuka, wanda hakan ke haifar musu da shiga mawuyacin hali wajen gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum, wanda hakan baya barin su zuwa gonakin su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp