Home Labarai ‘yan bindiga sun hallaka Mutane 4 a jihar Katsina

‘yan bindiga sun hallaka Mutane 4 a jihar Katsina

Taswirar Katsina
Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina ta tabbatar da mutuwar mutane hudu, inda takwas suka bata sakamakon harin ‘yan bindiga a wasu garuruwan jihar.

kakakin rundunar ASP Abubakar Aliyu ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce ‘yan bindigar sun aukawa wasu manoma a kayukan Dantsuntu da Nahuta a karamar hukumar batsari, in da suka hallaka mutane 4.

yayin da yake ganawa da manema labarai ASP ALiyu yace tuni rundunar ‘yan sanda ta sami labarin aukuwar lamari, haka kuma ya tabbatar da batan mutane 4 sakamakon harin ‘yan ta’addan.

wani daga cikin wadanda suka kubuta daga harin, wanda ya bukaci a sakaye sunan sa ya ce harin na daga cikin hare haren da ‘yan bindigar suke kaiwa kauyuka, wanda hakan ke haifar musu da shiga mawuyacin hali wajen gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum, wanda hakan baya barin su zuwa gonakin su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp