Home Labarai Emefiele ya cika ka’idar Beli

Emefiele ya cika ka’idar Beli

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya koma gida bayan ya cika sharuɗɗan belin da kotu ta ba shi.

Mai magana da yawun Gidan Yari na Kuje da ke Abuja, inda aka tsare Mista Emefiele, ya tabbatar da cewa an saki tsohon gwamnan a yammacin Juma’a.

Tun a ranar 22 ga watan Nuwamba ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da belinsa kan naira miliyan 300 tare da gabatar da mutum biyu da ke da kadarori a unguwar Maitama da ke birnin na Abuja. Haka nan, kotun ta umarce shi da miƙa mata dukkan takardunsa na tafiye-tafiye.

Lamarin na zuwa ne bayan wani rahoto da mai bincke na musamman, Jim Obazee, ya zarge shi da karya dokar kwangila da sayen kayayyakin gwamnati.

Rahoton Obazee, wanda Shugaba Bola Tinubu ya naɗa a watan Yuli don ya binciki CBN a ƙarƙashin mulkin Emefiele, ya zarge shi da amfani da wakilansa wajen sayen Bankin Union, da kuma yin amfani da ƙarfin ikonsa a cinikin bankunan Polaris da Keystone.

Gwamnatin Tinubu na zargin tsohon gwamnan wanda ta dakatar a watan Yuni da aikata almundahanar kuɗi naira biliyan 1.2, zargin da ya musanta.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp