harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

Wasu hare-haren ‘yan bindiga kan kauyuka sun yi sanadiyya mutuwar a kalla mutane 160 a tsakiyar Nijeriya a cewar mahukunta ranar litinin.

Adadin ya karu kan rahoton da rundunar sojin kasar ta fitar na cewa mutane 16 ne suka mutu a bias wani rikicin kabilanci da aka kwashe shekaru ana gudanarwa.

A yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na AFP shugaban karamar hukumar Bokkos, a jihar Filato, Monday Kassah ya ce an tabbatar da mutuwar mutane 113 a daren litinin.

Yace yan bindigar sun kai hari a kalla garuruwa 20 ma bambanta, inda suka taba gidajen al’ummar dake rayuwa a garuruwan a cewar, Kassah.

“Mun samu mutane sama da 300 da suka jikka” wadanda yanzu haka an kaisu asibitocin Bokkos, Jos da barkin ladi.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta red cross ta ce mutane 104 ne suka mutu a kauyuka 18 na Bokkos.

Haka kuma an ruwato cewa mutane 50 ne suka mutu a kauyu mabambanta dake karamar hukumar barkin ladi, kamar yadda Dickson Chollom, guda cikin ‘yan majalisar jihar.

Dickson yayi Allah wadai da harin, inda ya bukaci jami’an tsaro su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1184 days 3 hours 34 minutes 15 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1166 days 5 hours 15 minutes 40 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com