Home Labarai Mai Bincike CBN ya gayyaci Shugaban bankin Titan Trust

Mai Bincike CBN ya gayyaci Shugaban bankin Titan Trust

Mai Binciken Musamman kan badakalar Babban Bankin Najeriya, CBN, Jim Obazee, ya gayyaci Shugaban bankin Titan Trust Bank, Tunde Lemo da wasu mutum biyu masu hannayen jari a bankin, “domin wata ganawa” dangane da abin da ke tattare da sayen hannayen jarin kadarorin Bankin Union a shekarar 2022.

Ta cikin wata wasika da mai Bincike ya aika wa Tunde Lemo, sa’o’i kaɗan bayan ya fito ya ƙaryata zargin da ake yi masu.

Tunde dai tsohon Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Najeriya ne, kuma ana zargin rawar da ya taka wajen cinikin.

Cikin rahoton da Obazee ya damƙa wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, a ranar 20 Ga Disamba, ya bayyana cewa Lemo a lokacin da ya ke Mataimakin Gwamna ga Godwin Emefiele a CBN, ya yi amfani da maƙudan “kuɗaɗe ta hanyar haram” ta kafa bankin Titan Trust Bank, sannan ya yi amfani da kuɗaɗen ya saye Bankin Union da Keystone Bank, ta hanyar amfani da sunayen wasu ‘yan kamasho.

Obazee ya rubuta a cikin rahoton sa cewa Gwamnatin Tarayya ta gaggauta ƙwace TTB daga hannun Tunde, domin ya kafa bankin da kuɗaɗen da ya sata a CBN.

A martanin sa, Tunde Lemo ya yi bayani a ranar Lahadi cewa bankin sa ya bi ƙa’ida bai bauɗe ko kaɗan ba.

Cikin watan Oktoba ne SSS suka yi cacukui da A’isha, Mataimakiyar Gwamnan CBN, dangane da zargin karkatar da Dala Miliyan 300 zuwa Bankin Titan da Polaris.

Hukumar Tsaro ta SSS sun damƙe Mataimakiyar Gwamnan Babban Bankin Najeriya, CBN, A’isha Ahmed.

An kama ta ne dangane da hannun da ta ke da shi wajen yadda aka bi bauɗaɗɗiyar hanyar danƙara hannayen jari a bankunan Polaris Bank da Titan Bank, wato Union Bank na da.

Aisha Ahmad ita ce Mataimakiyar Gwamnan CBN mai lura da yawan kuɗaɗen hada-hada a bankuna.

Wani rahoto da gidan Talbijin din kasar na NTA ya bayyana cewa, ta na da hannu wajen yadda aka dauki Dala miliyan 300 a boye don sayen hannayen jari da bankin Polaris da bankin Titan, wato Union Bank a dai sauran su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp