Home Labarai harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

Wasu hare-haren ‘yan bindiga kan kauyuka sun yi sanadiyya mutuwar a kalla mutane 160 a tsakiyar Nijeriya a cewar mahukunta ranar litinin.

Adadin ya karu kan rahoton da rundunar sojin kasar ta fitar na cewa mutane 16 ne suka mutu a bias wani rikicin kabilanci da aka kwashe shekaru ana gudanarwa.

A yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na AFP shugaban karamar hukumar Bokkos, a jihar Filato, Monday Kassah ya ce an tabbatar da mutuwar mutane 113 a daren litinin.

Yace yan bindigar sun kai hari a kalla garuruwa 20 ma bambanta, inda suka taba gidajen al’ummar dake rayuwa a garuruwan a cewar, Kassah.

“Mun samu mutane sama da 300 da suka jikka” wadanda yanzu haka an kaisu asibitocin Bokkos, Jos da barkin ladi.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta red cross ta ce mutane 104 ne suka mutu a kauyuka 18 na Bokkos.

Haka kuma an ruwato cewa mutane 50 ne suka mutu a kauyu mabambanta dake karamar hukumar barkin ladi, kamar yadda Dickson Chollom, guda cikin ‘yan majalisar jihar.

Dickson yayi Allah wadai da harin, inda ya bukaci jami’an tsaro su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp