Home Labarai harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

Wasu hare-haren ‘yan bindiga kan kauyuka sun yi sanadiyya mutuwar a kalla mutane 160 a tsakiyar Nijeriya a cewar mahukunta ranar litinin.

Adadin ya karu kan rahoton da rundunar sojin kasar ta fitar na cewa mutane 16 ne suka mutu a bias wani rikicin kabilanci da aka kwashe shekaru ana gudanarwa.

A yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na AFP shugaban karamar hukumar Bokkos, a jihar Filato, Monday Kassah ya ce an tabbatar da mutuwar mutane 113 a daren litinin.

Yace yan bindigar sun kai hari a kalla garuruwa 20 ma bambanta, inda suka taba gidajen al’ummar dake rayuwa a garuruwan a cewar, Kassah.

“Mun samu mutane sama da 300 da suka jikka” wadanda yanzu haka an kaisu asibitocin Bokkos, Jos da barkin ladi.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta red cross ta ce mutane 104 ne suka mutu a kauyuka 18 na Bokkos.

Haka kuma an ruwato cewa mutane 50 ne suka mutu a kauyu mabambanta dake karamar hukumar barkin ladi, kamar yadda Dickson Chollom, guda cikin ‘yan majalisar jihar.

Dickson yayi Allah wadai da harin, inda ya bukaci jami’an tsaro su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp