Home General ‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a garin Kwapre dake karamar hukumar Hong ta jihar.

kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Sulaiman Ngureje ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar talata a birnin Yola.

inda ya ce lamarin ya auku ne ranar litinin, wato ranar da aka gudanar da bikin kirsimeti, sai dai ya ce har yanzu hukumar na gudanar da bincike bisa aukuwar lamarin.

 ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Babatola Afolabi, ya bayar da umarnin girke jami’an ‘yan sanda domin gudanar da bincike.

ya kuma bukaci al’umma da su tabbatar sun kai rahoton dukkan wani abu da basu yadda da shi ba ga hukumar da kuma dukkan saurarn hukumomin tsaro dake jihar dama kasa baki daya.

haka shima dagacin Dugwaba Mr Simon Buba,  ya tabbatar da faruwar lamarin, in da yace maharan sun hallaka mutane 2,

ya ce ana zargin maharan mambobin kungiyar tayar da kayar baya na  boko haram ne, da suka yiwa garin tsinke kan babura suka kuma yi awon gaba da kayan abinci suka nausa cikin dajin sambisa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp