Home General ‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

‘Yan Sanda Sun tabbatar da harin ‘yan Ta’adda a jihar Adamawa

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da harin ‘yan bindiga a garin Kwapre dake karamar hukumar Hong ta jihar.

kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Sulaiman Ngureje ne ya bayyana hakan ga manema labarai ranar talata a birnin Yola.

inda ya ce lamarin ya auku ne ranar litinin, wato ranar da aka gudanar da bikin kirsimeti, sai dai ya ce har yanzu hukumar na gudanar da bincike bisa aukuwar lamarin.

 ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Babatola Afolabi, ya bayar da umarnin girke jami’an ‘yan sanda domin gudanar da bincike.

ya kuma bukaci al’umma da su tabbatar sun kai rahoton dukkan wani abu da basu yadda da shi ba ga hukumar da kuma dukkan saurarn hukumomin tsaro dake jihar dama kasa baki daya.

haka shima dagacin Dugwaba Mr Simon Buba,  ya tabbatar da faruwar lamarin, in da yace maharan sun hallaka mutane 2,

ya ce ana zargin maharan mambobin kungiyar tayar da kayar baya na  boko haram ne, da suka yiwa garin tsinke kan babura suka kuma yi awon gaba da kayan abinci suka nausa cikin dajin sambisa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp