Home Labarai Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Kungiyar sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da kashe-kashen mutane da ake yi a jihar Filato, inda suka bukaci hukumomin da abin ya shafa su fara bincike.

Kakakin kungiyar, Sanata Suleiman Abdulrahman Kawu Sumaila a wata sanarwa da ya fitar, ya ce babu shakka Sanatocin Arewa sun yi Allah-wadai da munanan ayyukan kashe-kashe al’umma a jihar ta Filato.

Kawu ya kara da cewa, Sanatocin sun jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da ‘yan uwa, da jama’a, da kuma gwamnatin jihar Filato.

“Abun da ya faru tabbatar abun bacin rai ne, kuma mun tsaya tsayin daka kan kudurinmu na neman adalci. A matsayinmu na yan majalisa, muna yin Allah wadai da wannan mummunan aiki, muna kuma kira ga hukumomi da su gaggauta fara gudanar da cikakken bincike.

Bayar da kayan aikin da suka dace don gudanar da bincike da nufin ganowa da kuma kamo masu laifi shi ne mafi mahimmanci. Masu laifin dole ne su fuskanci hukuncin, tare da tabbatar da adalci.

a kara da cewa Sanatocin basu ji dadin faruwar wannan lamarin ba a cikin wannan mawuyacin yanayi, hadin kan ‘yan kasa na da matukar muhimmanci, yana mai cewa “a matsayinmu na wakilan jama’a, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta hada rahoton bincike na wannan lamari, ta kuma dauki matakin da ya dace don hana afkuwar hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp