Home Labarai Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Kungiyar sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da kashe-kashen mutane da ake yi a jihar Filato, inda suka bukaci hukumomin da abin ya shafa su fara bincike.

Kakakin kungiyar, Sanata Suleiman Abdulrahman Kawu Sumaila a wata sanarwa da ya fitar, ya ce babu shakka Sanatocin Arewa sun yi Allah-wadai da munanan ayyukan kashe-kashe al’umma a jihar ta Filato.

Kawu ya kara da cewa, Sanatocin sun jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da ‘yan uwa, da jama’a, da kuma gwamnatin jihar Filato.

“Abun da ya faru tabbatar abun bacin rai ne, kuma mun tsaya tsayin daka kan kudurinmu na neman adalci. A matsayinmu na yan majalisa, muna yin Allah wadai da wannan mummunan aiki, muna kuma kira ga hukumomi da su gaggauta fara gudanar da cikakken bincike.

Bayar da kayan aikin da suka dace don gudanar da bincike da nufin ganowa da kuma kamo masu laifi shi ne mafi mahimmanci. Masu laifin dole ne su fuskanci hukuncin, tare da tabbatar da adalci.

a kara da cewa Sanatocin basu ji dadin faruwar wannan lamarin ba a cikin wannan mawuyacin yanayi, hadin kan ‘yan kasa na da matukar muhimmanci, yana mai cewa “a matsayinmu na wakilan jama’a, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta hada rahoton bincike na wannan lamari, ta kuma dauki matakin da ya dace don hana afkuwar hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp