Home Labarai Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Sanatocin Nijeriya sun yi Alla wadai da harin jihar Filato

Kungiyar sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da kashe-kashen mutane da ake yi a jihar Filato, inda suka bukaci hukumomin da abin ya shafa su fara bincike.

Kakakin kungiyar, Sanata Suleiman Abdulrahman Kawu Sumaila a wata sanarwa da ya fitar, ya ce babu shakka Sanatocin Arewa sun yi Allah-wadai da munanan ayyukan kashe-kashe al’umma a jihar ta Filato.

Kawu ya kara da cewa, Sanatocin sun jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da ‘yan uwa, da jama’a, da kuma gwamnatin jihar Filato.

“Abun da ya faru tabbatar abun bacin rai ne, kuma mun tsaya tsayin daka kan kudurinmu na neman adalci. A matsayinmu na yan majalisa, muna yin Allah wadai da wannan mummunan aiki, muna kuma kira ga hukumomi da su gaggauta fara gudanar da cikakken bincike.

Bayar da kayan aikin da suka dace don gudanar da bincike da nufin ganowa da kuma kamo masu laifi shi ne mafi mahimmanci. Masu laifin dole ne su fuskanci hukuncin, tare da tabbatar da adalci.

a kara da cewa Sanatocin basu ji dadin faruwar wannan lamarin ba a cikin wannan mawuyacin yanayi, hadin kan ‘yan kasa na da matukar muhimmanci, yana mai cewa “a matsayinmu na wakilan jama’a, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta hada rahoton bincike na wannan lamari, ta kuma dauki matakin da ya dace don hana afkuwar hakan a nan gaba.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp