Lucky Aiyedatiwa ya karbi rantsuwa

An rantsar da gwamnan Ondo na riƙo, Lucky Aiyedatiwa a matsayin cikakken gwamnan jihar, sa’o’i kadan mutuwar Rotimi Akeredolu sanadin cutar kansar jini .

Mataimakin gwamnan, ya karɓi ragamar mulkin jihar a matakin riƙo, bayan Gwamna Rotimi Akeredolu ya aika wasiƙa ga majalisar dokokin jihar don sanar da ita game da ƙudurinsa na tafiya jinya da kuma miƙa ragamar mulkin jihar ga Lucky Aiyedatiwa.

Alƙalin alƙalan jihar Mai shari’a Olusegun Odusola ne ya rantsar da shi a ofishin gwamnan Ondo dake ciki birnin Akure.

Idan za’a Iya Tunawa Dai tun da farko, an yi ta dambarwa a fagen siyasar jihar, lokacin da majalisar dokokin Ondo ta fara yunƙurin tsige Lucky Aiyetadiwa daga kan kujerar mataimakin gwamna.

Sakataren gwamnan jihar da kwamishinonin Ondo da shugaban jam’iyyar APC da alƙalan jihar na cikin manyan jami’an da suka halarci taron rantsuwar.

PRNigeria hausa

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 43 minutes 14 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 24 minutes 39 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com