Home Labarai Tinubu ya maye gurbin TSA da CRF

Tinubu ya maye gurbin TSA da CRF

Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta rufe asusun ajiyar kudi na kasa wato (TSA) da gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi wajen tara kudaden shiga.

Sai dai gwamnatin tarayya ta umurci dukkan ma’aikatu, da hukumomi da su tura kashi 100 na kudaden shiga zuwa asusun ajiyar kudaden shiga na yau da kullun, wani bangare na asusun tattara kudaden shiga (CRF).

CRF shine sabon asusu inda a yanzu gwamnatin Tinubu za ta karba tare da hada kudaden shigarta a cikin sa.

Hakan ya zo ne bisa wata takardar mai kwanan watan 28 ga Disamba, 2023, wadda ma’aikatar kudi ta fitar a ranar Talata, 2 ga Janairu, 2024.

Wannan umarni dai ya rufe asusun baitul mali na bai daya da tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp