Home Labarai NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

NDLEA ta kama sama da mutane dubu 1 a Kano

Hukumar dake hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar Kano NDLEA, tace ta samu nasarar cafke mutane 1,016 da ake zargin su da tu’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekarar 2023 da muka yi bankwana da ita.

Mai magana da yawun hukumar Sadiq Muhammad Maigatari shi ne ya bayyana hakan, inda yace mutanen da aka kama sun hadar da mata guda 40.

Kazalika yace sun samu nasarar kama tan sama da 9,000 na miyagun kwayoyin duka dai a cikin shekarar.

Maigatari ya yaba da kokarin jami’an hukumar, inda yace suna daukar kwararan matakai wajen kawar da dukkanin wani nau’i na tu’ammali da miyagun kwayoyi a fadin Kano, domin samar wa da al’ummar jihar zaman lafiya da kwanciyar hankali.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp