Home Labarai Za mu bi diddigin yadda za’a kashe kasafin 2024 – Tinubu

Za mu bi diddigin yadda za’a kashe kasafin 2024 – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya sa hannu kan ƙudurin kasafin kuɗin bana na sama da naira tirliyan 28 zuwa doka, jim kaɗan bayan komawarsa Abuja daga Lagos.

Ya dai bai wa al’ummar Najeriya tabbacin cewa zai bi diddigi wajen ganin yadda ake aiwatar da kasafin kuɗin, ya kuma ce ya umarci dukkan ma’aikatu da hukumomi su riƙa bayar da rahoton yadda suke aiwatar da kasafin kuɗin wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban Najeriya shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai Ajuri Ngelale ya fitar ta ce manyan ɓangarorin da kasafin kuɗin ya mayar da hankali a kansu akwai tsaron ƙasa da samar da tsaro a cikin gida, samar da aikin yi da daidaita harkokin tattalin arziƙi da bunƙasa yanayin zuba jari da rage talauci.

Shugaba Tinubu ya nanata cewa ƙudurinsa na kyautata harkokin zuba jari da ƙoƙarin samar da al’umma mai bin doka wadda ba za ta fifita kowanne mutum ba, zai fara da muhimman sauye-sauye a ɓangaren shari’a, wanda kuma an samar da kuɗaɗen yin su a cikin kasafin kuɗin.

“Samar da kuɗi ga ɓangaren shari’a wani muhimmin ƙuduri ga ƙoƙarinmu wajen tabbatar da wata al’umma mai bin doka da tsayawa a kan daidai. An ƙara kuɗaɗen da ake warewa ɓangaren shari’a daga tushe daga naira biliyan 165 zuwa naira biliyan 342,” cewar shugaban ƙasar.

Sanarwar ta ce muhimman alƙaluma a cikin kasafin kuɗin su ne manyan ayyuka naira tirliyan goma da ayyukan yau da kullum naira tirliyan 8.8 sai biyan basuka tirliyan naira 8.2 sai kason tallafi na doka daga asusun tarayya naira tirliyan 1.7.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp