Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Harin rundunar sojin saman Nijeriya yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda masu tayar da kayar baya a dajin Sambisa da ke yankin tafkin chadi tare da hallaka mayakan 12.

Ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fita mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Janairu 2024.

Sanarwar ta ce a kokarin rundunar sojin na kakkabe matsalolin rashin tsaron a yankin arewa maso gabashin kasar, rundunar na cigaba da samun nasara, in da a ranar 5 ga watan janairun wannan shekara rundunar ta sami nasara a Parisu bayan wani bayanan sirri da ta samu na yadda ‘yan ta’adda ke karakaina da makamai da alburusai a yankin.

Parisu wani yanki ne dake kusa da dajin sambisa, wanda ‘yan ta’adda suka taba mamaye shi, sai dai daga bisani sojojin Nijeriya suka, harin da ya yi sanadiyya mutuwar mayakn da dama tare da kwace maboyar ta su.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa ‘yan ta’adda 12 aka hallaka yayin harin dakarun ta sama, tare da tarwatse maboyar su, harin kuma ya dakile yunkurin ‘yan bindigar na kai hari kan dakarun sojojin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 16 hours 45 minutes 4 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 18 hours 26 minutes 29 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com