Home Labarai Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Harin rundunar sojin saman Nijeriya yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda masu tayar da kayar baya a dajin Sambisa da ke yankin tafkin chadi tare da hallaka mayakan 12.

Ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fita mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Janairu 2024.

Sanarwar ta ce a kokarin rundunar sojin na kakkabe matsalolin rashin tsaron a yankin arewa maso gabashin kasar, rundunar na cigaba da samun nasara, in da a ranar 5 ga watan janairun wannan shekara rundunar ta sami nasara a Parisu bayan wani bayanan sirri da ta samu na yadda ‘yan ta’adda ke karakaina da makamai da alburusai a yankin.

Parisu wani yanki ne dake kusa da dajin sambisa, wanda ‘yan ta’adda suka taba mamaye shi, sai dai daga bisani sojojin Nijeriya suka, harin da ya yi sanadiyya mutuwar mayakn da dama tare da kwace maboyar ta su.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa ‘yan ta’adda 12 aka hallaka yayin harin dakarun ta sama, tare da tarwatse maboyar su, harin kuma ya dakile yunkurin ‘yan bindigar na kai hari kan dakarun sojojin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp