Home Labarai Sojoji sun hallaka jagoran ISWAP a jihar Borno

Sojoji sun hallaka jagoran ISWAP a jihar Borno

Dakarun sojin saman Nijeriya sun sami nasarar hallaka jagoran mayakan ISWAP Ba’a Shuwa a jihar Borno.

Harin na ranar talata yayi sanadiyar mutuwar mayakan na ISWAP da dama sun.
Zagazola Makama mai bincike kan lamurran da suka shafi tsaro a yankin tafkin Chadi, ya ruwaito cewa harin da yayi sanadiyar Shuwa ya auku ne a Kwatan Dilla, dake karamar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Yace hotuna sun nuna yadda gawarwakin mayakan da aka hallaka ke kwance.
Mayakan dai na boye a wata maboyar su domin gujewa luguden wuta da sojojin ke yi a yankin Timbuktu triangle.

Shuwa ya zama jagoran ISWAP a shekarar 2021, bayan mutuwar Abubakar Shekau.
Haka Kuma ya jagoranci gudanar da ayyukan ta’addanci Chiralia, Markas Kauwa, Abirma, Buk, Abulam, Dusula, Abbagajiri, Gorgore da sauran yankuna da dama na Timbuktu da Alagarno a jihar Borno.

Shuwa da tawagar sa na da alhakin hare-haren bama bamai a garuruwan Damaturu-Maiduguri, Askira, Buratai, Buni Yadi, Buni Gari, Gaidam da sauran yankunan dake jihohin Borno da Yobe.

PRNigeria hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp