Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kubutar da mutane 19 a jihohin Katsina da Zamfara

Sojojin Nijeriya sun kubutar da mutane 19 a jihohin Katsina da Zamfara

Dakarun sojin Najeriya na rundunar Hadarin Daji sun sami nasarar kai wa ‘yan ta’adda farmaki tare da kubutar da mutum tara da aka yi garkuwa da su, sun kuma gano makamai da albarusai, da babur da na’urorin sadarwa.

A ranar Alhamis, runduna ta takwas ta sojin Najeriya ce ta yi wannan aikin karkashin jagorancin Manjo Janar Godwin Mutkut, a karamar hukumar Batsari da Safana da ke jihar Katsina a arewacin Najeriya inda aka kashe ‘yan ta’adda 10 yayin da wasu da dama suka tsere da munanan raunuka.

Sanarwar da rundunar sojin ta fitar ta ce ta samu bindiga kirar AK-47, da alburusai da bindigogi kirar gida guda uku da harba-ruga bakwai da sauran da sauran bindigogi masu hatsari da na’urorin sadarwa da wayoyin hannu da kakin soji tare da babura hudu.

Haka kuma sanarwar ta ce a wannan ranar ce dai kuma dakarun soji na rundunar HADARIN DAJI da ke aiki a jihar Zamfara suka kai samame kauyukan Dansadau da Dandalla a karamar hukumar Maru, inda suka kubutar da mutum tara da ake garkuwa da su da suka hadar da mata biyar da jarirai hudu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ‘yan bindigar sun gudu ne suka bar mutanen bayan musayar da jami’an tsaro.

Tuni aka sada mutanen da iyalansu a garin Magami kamar yadda sanarwar ta bayyana.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp