Home Labarai Sojojin Nijeriya sun kubutar da mutane 19 a jihohin Katsina da Zamfara

Sojojin Nijeriya sun kubutar da mutane 19 a jihohin Katsina da Zamfara

Dakarun sojin Najeriya na rundunar Hadarin Daji sun sami nasarar kai wa ‘yan ta’adda farmaki tare da kubutar da mutum tara da aka yi garkuwa da su, sun kuma gano makamai da albarusai, da babur da na’urorin sadarwa.

A ranar Alhamis, runduna ta takwas ta sojin Najeriya ce ta yi wannan aikin karkashin jagorancin Manjo Janar Godwin Mutkut, a karamar hukumar Batsari da Safana da ke jihar Katsina a arewacin Najeriya inda aka kashe ‘yan ta’adda 10 yayin da wasu da dama suka tsere da munanan raunuka.

Sanarwar da rundunar sojin ta fitar ta ce ta samu bindiga kirar AK-47, da alburusai da bindigogi kirar gida guda uku da harba-ruga bakwai da sauran da sauran bindigogi masu hatsari da na’urorin sadarwa da wayoyin hannu da kakin soji tare da babura hudu.

Haka kuma sanarwar ta ce a wannan ranar ce dai kuma dakarun soji na rundunar HADARIN DAJI da ke aiki a jihar Zamfara suka kai samame kauyukan Dansadau da Dandalla a karamar hukumar Maru, inda suka kubutar da mutum tara da ake garkuwa da su da suka hadar da mata biyar da jarirai hudu.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ‘yan bindigar sun gudu ne suka bar mutanen bayan musayar da jami’an tsaro.

Tuni aka sada mutanen da iyalansu a garin Magami kamar yadda sanarwar ta bayyana.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp