Home Labarai Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Sojojin saman Nijeriya sun hallaka ‘yan boko haram 12 a Sambisa

Harin rundunar sojin saman Nijeriya yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar ‘yan ta’adda masu tayar da kayar baya a dajin Sambisa da ke yankin tafkin chadi tare da hallaka mayakan 12.

Ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fita mai dauke da kwanan watan 7 ga watan Janairu 2024.

Sanarwar ta ce a kokarin rundunar sojin na kakkabe matsalolin rashin tsaron a yankin arewa maso gabashin kasar, rundunar na cigaba da samun nasara, in da a ranar 5 ga watan janairun wannan shekara rundunar ta sami nasara a Parisu bayan wani bayanan sirri da ta samu na yadda ‘yan ta’adda ke karakaina da makamai da alburusai a yankin.

Parisu wani yanki ne dake kusa da dajin sambisa, wanda ‘yan ta’adda suka taba mamaye shi, sai dai daga bisani sojojin Nijeriya suka, harin da ya yi sanadiyya mutuwar mayakn da dama tare da kwace maboyar ta su.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa ‘yan ta’adda 12 aka hallaka yayin harin dakarun ta sama, tare da tarwatse maboyar su, harin kuma ya dakile yunkurin ‘yan bindigar na kai hari kan dakarun sojojin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp