Jam’iyyar APC a jihar Kano ta ce ta Karfi Kaddara

Jam’iyyar APC a Kano sun tace sun rungumi ƙaddara game da hukuncin kotun kolin Najeriya da ta tabbatar da nasarar Gwamna Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP.

Sakataren jam’iyyar na jiha Ibrahim Zakari Sarina, ne ya bayyana haka ta cikin wata hira da gudanar da kafar yada labarai ta BBC, in da ya ce sun karɓi ƙaddara, suna kuma fatan hakan ya zame musu alkairi.

”Allah ya sa hakan ne ya fi alkari, kuma muna bai wa ‘yan jam’iyar mu na APC da sauran al’ummar jihar kano hakuri, tare da kiran a zauna lafiya”, in ji shi.

Ya ce kuma suna kyautata wa Allah zato cewa tabbas hakan zai zama alkairi a gare su.

”A yanzu muna cikin alhini, kuma bai kamata mu ɗauki mataki a lokacin alhini ba, amma idan ƙura ta lafa, za mu zo mu zauna, mu shirya domin tunkarar zaɓen 2027”.

Tun da farko dai jam’iyyar ce ta yi nasara a kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara, kafin yau kotun ƙoli ta yi watsi da hukunce-hukuncen kotunan farkon.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 15 hours 27 minutes 50 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 17 hours 9 minutes 15 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com