Home Labarai EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

Hukumar EFCC ta sake waiwayar binciken halasta kuɗaɗen haram na wasu tsofaffin gwamnoni 12 da wasu ministoci da suka gabata, kuma adadin kuɗin ya haura naira biliyan 853.b.

Jaridar Punch ta gano cewa adadin kuɗin da ake nema daga wajen wasu manyan tsofaffin minisrtoci da gwamnoni ya kai naira bilyan 772.2, kuma a yanzu haka EFFC na ci gaba da bincike kan naira bilyan 81.6 wanda ake tsammanin an sace su a ma’aikatar agajin gaggawa da yaki talauci.

Kazalika, kazalika ana zargin wasu dala biliyan biyi da ake zargin sun bata ta hanyar halasta kuɗin haram, wadanda ake tsammanin an karkatar da su ne a baya-bayan nan.

Akwai kuma dala biliyn 2.2 da ake zargin tsohon mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Sambo Dasuki ya karkatar da su, da mai gidajen yaɗa labara nan da ya rasu Raymond Dokpesi; da tsohon gwamnan Sokoto Attahiru Bafarawa: Tsohon ministan kudi Bashir Yuguda da sauransu.

A cewar EFCC kudaden an ware su ne domin sayan makamai da za su taimakwa yaƙin da ake da ‘yan tada ƙayar baya, amma aka sace su aka karkatar da sy aka kashe ba ta hanyar da ta dace ba.

Yayin da Dasuki ke a tsare a DSS a 2015, EFCC ta kama Dokpesi da Bafarawa da Yuguda da dai sauransu..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp