Home Labarai EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

Hukumar EFCC ta sake waiwayar binciken halasta kuɗaɗen haram na wasu tsofaffin gwamnoni 12 da wasu ministoci da suka gabata, kuma adadin kuɗin ya haura naira biliyan 853.b.

Jaridar Punch ta gano cewa adadin kuɗin da ake nema daga wajen wasu manyan tsofaffin minisrtoci da gwamnoni ya kai naira bilyan 772.2, kuma a yanzu haka EFFC na ci gaba da bincike kan naira bilyan 81.6 wanda ake tsammanin an sace su a ma’aikatar agajin gaggawa da yaki talauci.

Kazalika, kazalika ana zargin wasu dala biliyan biyi da ake zargin sun bata ta hanyar halasta kuɗin haram, wadanda ake tsammanin an karkatar da su ne a baya-bayan nan.

Akwai kuma dala biliyn 2.2 da ake zargin tsohon mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Sambo Dasuki ya karkatar da su, da mai gidajen yaɗa labara nan da ya rasu Raymond Dokpesi; da tsohon gwamnan Sokoto Attahiru Bafarawa: Tsohon ministan kudi Bashir Yuguda da sauransu.

A cewar EFCC kudaden an ware su ne domin sayan makamai da za su taimakwa yaƙin da ake da ‘yan tada ƙayar baya, amma aka sace su aka karkatar da sy aka kashe ba ta hanyar da ta dace ba.

Yayin da Dasuki ke a tsare a DSS a 2015, EFCC ta kama Dokpesi da Bafarawa da Yuguda da dai sauransu..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp