Home Labarai Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Tinubu Ya gana da Hafsoshin tsaron Kasar kan matsalar Tsaro

Shugaban Nijeriya Asiwajo Bola Tinubu ya gana da hafsoshin tsaron kasar da kuma wasu manyan hukumomin tsaro a fadarsa da ke birnin tarayya Abuja, a ranar Talata.

Hafsoshin tsaron da suka halarci ganawar sun haɗa da babban hafsan tsaro, Janar Christopher Musa, shugaban rundunar sojin ƙasa, Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, shugaban sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar, da kuma shugaban sojojin ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ogalla.

haka kuma mai taimakawa shugaban ƙasa kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu na cikin waɗanda suka halarci taron.

Sun tattauna kan batun karuwar aikata ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma kashe-kashe a faɗin kasar da nufin magance su.

Nijeriya dai na guda cikin kasashen yammacin Afirka dake fama da matsalar rashin tsaro, kama daga masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa dake cin karensu babu babbaka a yankin Arewa maso yamma da wasu jihohi a tsakiyar kasar.

sai kuma mayakan boko haram da na ISWAP dake tayar da kayar baya a yakin arewa maso Gabas, sai Kudu maso kudu da wasu yankuna a kudancin kasar dake fama da mayakan IPOB masu rajin kafa kasar Biyafara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp