Home Labarai NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

Hukumar sadarwa ta Najeriya – NCC ta dakatar da shirin ta na hana masu amfani da layin kamfanin Glo kiran layukan kamfanin MTN na tsawon kwanaki ashirin ɗaya.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, Daraktan hulda da jama’a na hukumar NCC, Reuben Mouka, ya ce hukumar ta yanke shawarar dakatar da matakin ne bayan da kamfanonin sadarwa suka amince da warware duk wadansu matsalolin da ke tsakaninsu.

Tun da farko dai, hukumar ta ce ta amince da kamfanin MTN ya fara yanke kira da layin kamfanin Globacom daga ranar 18 ga Janairu, 2024, saboda takaddamar bashin da ya daɗe a tsakanin ɓangarorin.

“Hukumar ta yi farin cikin sanar da cewa a yanzu kamfanonin MTN da Glo sun cimma matsaya don warware duk wata matsala da ke tsakaninsu, saboda haka, hukumar ta dage dakatarwar da aka yi na tsawon kwanaki 21 daga yau 17 ga Janairu, 2024.

“A wajen bayar da amincewar hukumar, hukumar tana sane da illolin da shawarar za ta iya haifarwa ga masu amfani kamfanonin sadarwar biyu, don haka ta ci gaba da jan hankalin bangarorin biyu don saukaka wani kuduri wanda ya ba da fifiko da kuma kare muradun mabukaci da kuma tafiyar da harkokin sadarwa ta kasa baki daya,” in ji NCC.

“Yayin da hukumar ke sa ran MTN da Glo za su warware duk wata matsala da ta kunno kai a cikin kwanaki 21, hukumar ta ce dole ne duk kamfanonin da ke aiki su warware basussuka a matsayin wani abin da ya dace don bin ka’idojin doka na duk masu lasisi.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp