Home Labarai NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

NCC ta dakatar da shirin hana masu layin Glo kiran layin MTN

Hukumar sadarwa ta Najeriya – NCC ta dakatar da shirin ta na hana masu amfani da layin kamfanin Glo kiran layukan kamfanin MTN na tsawon kwanaki ashirin ɗaya.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, Daraktan hulda da jama’a na hukumar NCC, Reuben Mouka, ya ce hukumar ta yanke shawarar dakatar da matakin ne bayan da kamfanonin sadarwa suka amince da warware duk wadansu matsalolin da ke tsakaninsu.

Tun da farko dai, hukumar ta ce ta amince da kamfanin MTN ya fara yanke kira da layin kamfanin Globacom daga ranar 18 ga Janairu, 2024, saboda takaddamar bashin da ya daɗe a tsakanin ɓangarorin.

“Hukumar ta yi farin cikin sanar da cewa a yanzu kamfanonin MTN da Glo sun cimma matsaya don warware duk wata matsala da ke tsakaninsu, saboda haka, hukumar ta dage dakatarwar da aka yi na tsawon kwanaki 21 daga yau 17 ga Janairu, 2024.

“A wajen bayar da amincewar hukumar, hukumar tana sane da illolin da shawarar za ta iya haifarwa ga masu amfani kamfanonin sadarwar biyu, don haka ta ci gaba da jan hankalin bangarorin biyu don saukaka wani kuduri wanda ya ba da fifiko da kuma kare muradun mabukaci da kuma tafiyar da harkokin sadarwa ta kasa baki daya,” in ji NCC.

“Yayin da hukumar ke sa ran MTN da Glo za su warware duk wata matsala da ta kunno kai a cikin kwanaki 21, hukumar ta ce dole ne duk kamfanonin da ke aiki su warware basussuka a matsayin wani abin da ya dace don bin ka’idojin doka na duk masu lasisi.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp