Home Labarai Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar masu garkuwa da mutane a Taraba

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar masu garkuwa da mutane a Taraba

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa dakarun rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro, sun lalata wata maboyar masu garkuwa da mutane tare da kuɓutar da mutum huɗu da aka yi garkuwa da su a yankin ƙaramar hukumar Yorro na jihar Taraba.

Cikin wata sanarwa da mai riƙon muƙamin daraktan yaɗa labaran rundunar sojin Najeriya ta 6 da ke jihar, Laftanar Oni Olubodunde ya sanya wa hannu, ya ce sojojin sun ƙaddamar da yaƙi da ‘yan bindigar ne tun da suka yawaita kai hare-hare a yankin ƙaramar hukumar.

Ya ƙara da cewa dakarunsu sun yi gumurzu da masu garkuwar a tsaunukan Gampu da na Ban Yorro, bayan musayar wuta tsakanin ɓangarorin ne, sai ‘yan bindigar suka arce inda suka bar mutum huɗu da suka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin za su ci gaba da aiki a yankin har sai sun tabbatar da kuɓutar da sauran mutanen da ke hannun masu garkuwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp