Home Labarai Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin NNPC yace bazai kara kudin man Fetur a Nijeriya ba

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya ce ba shi da shirin kara farashin man fetur a kasar duk kuwa kara tabarbarewar darajar takardar kudin Naira da ya haddasa tsadar rayuwa.

Karo na biyu kenan da Najeriyar ke karya darajar kudinta cikin kasa da shekara guda, lamarin da ya haddasa hauhawar farashin kayayyaki kari kan matsin rayuwar da jama’a ke fuskanta tun tuni, kuma wannan batu ya sanya fargabar karuwar farashin man na fetur, batun da kamfanin na NNPC ke cewa babu wannan shirin a yanzu.

Sanarwar ta NNPC na zuwa a dai dai lokacin da kiraye-kiraye ke ci gaba da tsananta daga kungiyoyi wajen ganin gwamnatin Najeriyar ta dauki matakan kawo sassauci kan matsin rayuwar da ake ciki, wadannan kungiyoyi kuwa har da na kwadago da suka bayar da wa’adin makwanni biyu ko kuma tsunduma yajin aiki.

A bangare guda kungiyar gwamnonin Najeriyar ta aikewa da gwamnatin tarayya bukatar gaggawa wajen magance matsalar ta tsadar rayuwa baya ga daidaita farashin Naira da kuma uwa uba magance matsalolin tsaron da arewacin kasar ke fama da shi.

A hukumance dai yanzu ana sayar da duk dalar Amurka guda kan Nairar Najeriyar dubu 1 da 531 sabanin 900 da ake sayarwa a makwannin baya, lamarin da ya sake tsawwala tsadar rayuwar da al’umma kef ama da shi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp