Home Labarai Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta hana gwamnatin jihar ci gaba da rusa gine-ginen da ke unguwar Salanta wanda tun farko ta sanya musu alama.

A yayin da yake yanke hukunci, Mai shari’a Simon Amobeda, ya bayyana cewa gine-ginen an mallake su ne bisa ka’ida, don haka ba za a iya rushe su ba tare da amincewar masu su ba.

Masu shigar da kara sun garzaya kotu ne a watan Yulin 2023, suna neman ta kare musu hakkinsu na kadarorin da suka mallaka, amma gwamnatin jihar ta sanya musu alamar rugujewa.

 

A lokacin ne kotun ta ba da umarnin wucin gadi da ke hana gwamnatin jihar daukar mataki har sai an yanke hukuncin karshe.

Wadanda suka shigar da karar sun hada da Alhaji Ali Mai kusa da Ali Rabiu Awwalu da Balarabe Sani Salanta da Umar Ibrahim Batayya da Salisu Idris Daneji da Alhaji Ibrahim Sadi da Umar Shittu Sharubutu.

Lauyan masu kara Kabiru Ishaq Kofa ya ce bisa ga hukuncin da kotun ta yanke, “Gwamnatin Kano ko hukumar raya birane ta jihar (KANUPDA), ko wakilansu, har abada an hana su hari ko rushewa ko ma kwace gine-ginen ba tare da amincewar masu su ba”.

Lauyan ya ce wadanda yake karewa sun bi duk matakan shari’a kafin su mallaki kadarorin tun kafin zuwan wannan gwamnati.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin rusa wasu gine-gine da ake zargin mallakarsu ba bisa ka’ida ba ne kwanaki kadan bayan hawansa mulki.

Gwamnan ya zargi gwamnatin da ta gabata da bayar da filaye ga wasu ’yan baranda da kuma sayar da wasu filaye na makarantun gwamnati da makabartu da masallatai ba tare da bin ka’ida ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp