Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta bayyana dalilin rufe kantin Sahad na Abuja

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana dalilin rufe kantin Sahad na Abuja

Awa 24 bayan shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana hanyoyin dakile matsalar karancin abinci da tsadarsa a kasar, jami’an hukumar da ke kare muradan masu saye ta kasa sun rufe, babban shagon nan na Sahad Stores da ke yankin Area 11 a Abuja.

An dai zargin cewa masu gkatafaren shagon da kara wa abokan huldarsu kudin kaya fiye da farashin da ke makale a jikin kayan.

Da yake yi wa ‘yan jarida bayani, shugaban hukumar mai kare muradan masu saye ta kasa, Adamu Ahmed Abdullahi ya ce wani bincike da hukumar ta gudanar kan katafaren shagon ya nuna musu yadda masu gudanar wa shagon suke “cutar” masu saye.

Ya kara da cewa shagon zai ci gaba da kasancewa a rufe har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

“ Mun fahimci cewa mutanen nan abun da suke yi yaudara ne inda babu gaskiya da yin abu a faifai dangane da farashin kayan da suke da su wanda kuma hakan ya yi karo da sashe na (135) da dokar da ta hana a yaudari abokin hulda ta hanyar cea ka da mai saye ya biya kudin kaya fiye da abin da ke rubuce a kan kayan.” In ji Adamu Ahmed Abdullahi.

PRNijeriya hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp