Home Labarai Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta hana gwamnatin jihar ci gaba da rusa gine-ginen da ke unguwar Salanta wanda tun farko ta sanya musu alama.

A yayin da yake yanke hukunci, Mai shari’a Simon Amobeda, ya bayyana cewa gine-ginen an mallake su ne bisa ka’ida, don haka ba za a iya rushe su ba tare da amincewar masu su ba.

Masu shigar da kara sun garzaya kotu ne a watan Yulin 2023, suna neman ta kare musu hakkinsu na kadarorin da suka mallaka, amma gwamnatin jihar ta sanya musu alamar rugujewa.

 

A lokacin ne kotun ta ba da umarnin wucin gadi da ke hana gwamnatin jihar daukar mataki har sai an yanke hukuncin karshe.

Wadanda suka shigar da karar sun hada da Alhaji Ali Mai kusa da Ali Rabiu Awwalu da Balarabe Sani Salanta da Umar Ibrahim Batayya da Salisu Idris Daneji da Alhaji Ibrahim Sadi da Umar Shittu Sharubutu.

Lauyan masu kara Kabiru Ishaq Kofa ya ce bisa ga hukuncin da kotun ta yanke, “Gwamnatin Kano ko hukumar raya birane ta jihar (KANUPDA), ko wakilansu, har abada an hana su hari ko rushewa ko ma kwace gine-ginen ba tare da amincewar masu su ba”.

Lauyan ya ce wadanda yake karewa sun bi duk matakan shari’a kafin su mallaki kadarorin tun kafin zuwan wannan gwamnati.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin rusa wasu gine-gine da ake zargin mallakarsu ba bisa ka’ida ba ne kwanaki kadan bayan hawansa mulki.

Gwamnan ya zargi gwamnatin da ta gabata da bayar da filaye ga wasu ’yan baranda da kuma sayar da wasu filaye na makarantun gwamnati da makabartu da masallatai ba tare da bin ka’ida ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp