Home Labarai Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Kotu ta haramtawa Abba gida gida Rusau a jihar Kano

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta hana gwamnatin jihar ci gaba da rusa gine-ginen da ke unguwar Salanta wanda tun farko ta sanya musu alama.

A yayin da yake yanke hukunci, Mai shari’a Simon Amobeda, ya bayyana cewa gine-ginen an mallake su ne bisa ka’ida, don haka ba za a iya rushe su ba tare da amincewar masu su ba.

Masu shigar da kara sun garzaya kotu ne a watan Yulin 2023, suna neman ta kare musu hakkinsu na kadarorin da suka mallaka, amma gwamnatin jihar ta sanya musu alamar rugujewa.

 

A lokacin ne kotun ta ba da umarnin wucin gadi da ke hana gwamnatin jihar daukar mataki har sai an yanke hukuncin karshe.

Wadanda suka shigar da karar sun hada da Alhaji Ali Mai kusa da Ali Rabiu Awwalu da Balarabe Sani Salanta da Umar Ibrahim Batayya da Salisu Idris Daneji da Alhaji Ibrahim Sadi da Umar Shittu Sharubutu.

Lauyan masu kara Kabiru Ishaq Kofa ya ce bisa ga hukuncin da kotun ta yanke, “Gwamnatin Kano ko hukumar raya birane ta jihar (KANUPDA), ko wakilansu, har abada an hana su hari ko rushewa ko ma kwace gine-ginen ba tare da amincewar masu su ba”.

Lauyan ya ce wadanda yake karewa sun bi duk matakan shari’a kafin su mallaki kadarorin tun kafin zuwan wannan gwamnati.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin rusa wasu gine-gine da ake zargin mallakarsu ba bisa ka’ida ba ne kwanaki kadan bayan hawansa mulki.

Gwamnan ya zargi gwamnatin da ta gabata da bayar da filaye ga wasu ’yan baranda da kuma sayar da wasu filaye na makarantun gwamnati da makabartu da masallatai ba tare da bin ka’ida ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp