Gwamnatin Nijeriya ta bayyana dalilin rufe kantin Sahad na Abuja

Awa 24 bayan shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana hanyoyin dakile matsalar karancin abinci da tsadarsa a kasar, jami’an hukumar da ke kare muradan masu saye ta kasa sun rufe, babban shagon nan na Sahad Stores da ke yankin Area 11 a Abuja.

An dai zargin cewa masu gkatafaren shagon da kara wa abokan huldarsu kudin kaya fiye da farashin da ke makale a jikin kayan.

Da yake yi wa ‘yan jarida bayani, shugaban hukumar mai kare muradan masu saye ta kasa, Adamu Ahmed Abdullahi ya ce wani bincike da hukumar ta gudanar kan katafaren shagon ya nuna musu yadda masu gudanar wa shagon suke “cutar” masu saye.

Ya kara da cewa shagon zai ci gaba da kasancewa a rufe har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

“ Mun fahimci cewa mutanen nan abun da suke yi yaudara ne inda babu gaskiya da yin abu a faifai dangane da farashin kayan da suke da su wanda kuma hakan ya yi karo da sashe na (135) da dokar da ta hana a yaudari abokin hulda ta hanyar cea ka da mai saye ya biya kudin kaya fiye da abin da ke rubuce a kan kayan.” In ji Adamu Ahmed Abdullahi.

PRNijeriya hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 15 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 57 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com