• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Labarai dalilin ECOWAS na Janye takunkumi kan Kasashen Nijar, Mali, Burkina Faso da...
  • Labarai

dalilin ECOWAS na Janye takunkumi kan Kasashen Nijar, Mali, Burkina Faso da Guinea

By
Burkina Faso, Ecowas, Guinea, Mali, Nijar
-
February 24, 2024
Arewa Award

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzkin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta ɗage tarin takunkuman da ta ƙaƙaba wa ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Guinea.

Ƙungiyar ta ɗauki matakin ne a wani taron shugabannin ƙasashen ƙungiyar da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya.

Ƙungiyar ta ce a yanzu za ta iya gayyatar ƙasashen huɗu zuwa tarukanta da suka shafi tsaro da zaman lafiya.

Ecowas ta ce ɗage takunkuman – wanda zai fara aiki nan take – ta yi shi ne bisa dalilai na jin kai.

Huka kuma ƙungiyar ta jaddada kiranta na sakin hamɓararreb shugaban Nijar Mohamed Bazaoum da sojojin ƙasar ke ci gaba da yi wa ɗaurin talala.

Ecowas ta kaƙaba wa ƙasashe takunkuman ne bayan da sojoji suka kifar da gwamnatocin fara hula a ƙasashen.

Daga cikin takunkuman da ƙungiyar ta ƙaƙaba wa ƙasashen sun haɗa da rufe iyakokin ƙasashen da na ƙungiyar da kuma yanke wutar lantarki a Nijar da sauran takunkuman karya tattalin arziki.

Read Also:

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

A makonnin baya-bayan ne ƙasashen Nijar, MAli da Burkina Faso suka ayyana ficewa daga ƙungiyar bayan da suka zargi ƙungiyar Ecowas da ƙaƙaba musu takunkuman karya tattalin arziki.

Ecowas ta riƙa fuskantar matsin lamba daga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane kan ta ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Ko a makon da ya gabata ma tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya Janar Yakubu Gowan wanda shi ne mutum ɗaya tilo da ya rage cikin shugabanin da suka kafa ƙungiyar, ya yi kira ga shugabanninta da su ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Nijar ta samu kanta cikin takunkuman Ecowas bayan da sojojin kasar suka kifar da gwamnatin farar hula da Mohamed Bazoum cikin watan Yulin shekarar da ta gabata.

Dama dai masu sharhi sun daɗe suna ta kiraye-kiraye ga shugabannin ƙungiyar su yi kaffa-kaffa, su mai da hankali wajen lalamar ‘ya’yan kungiyar idan ba haka ba garin gyaran gira a rasa ido.

Duk da cewa tun da farko shugabannin kungiyar Ecowas ɗin sun cije a kan matsayinsu na dakatar da kasashen da suka bijire wa demokuradiyyar tare da sanya musu takunkumi,

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleGwamnatin Nijeriya ta sake bude kantin Sahad na Abuja
Next article‘Yan bindiga sun yi awon gaba da dalibai sama da 100 a jihar Kaduna
Burkina Faso, Ecowas, Guinea, Mali, Nijar

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi

An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro

Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

karo na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewa

Matatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100

Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban bara

Ana tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano – Gwamnati

JOHESU – Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma’aikatan asibiti

Gwamnan Kano zai koma Jam’iyyar APC

Gwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan Siyasa

Jam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPP

Recent Posts

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar
  • Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro
  • Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1687 days 17 hours 48 minutes 57 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1669 days 19 hours 30 minutes 22 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a KadunaBa a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya - Sanata NingiAn ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin NijarTurkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar TsaroNajeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasarkaro na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewaMatatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban baraAna tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano - GwamnatiJOHESU - Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma'aikatan asibitiGwamnan Kano zai koma Jam'iyyar APCGwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci
X whatsapp