• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Labarai dalilin ECOWAS na Janye takunkumi kan Kasashen Nijar, Mali, Burkina Faso da...
  • Labarai

dalilin ECOWAS na Janye takunkumi kan Kasashen Nijar, Mali, Burkina Faso da Guinea

By
Burkina Faso, Ecowas, Guinea, Mali, Nijar
-
February 24, 2024
Arewa Award

Ƙungiyar Raya Tattalin Arzkin Ƙasashen Afirka ta Yamma, Ecowas ta ɗage tarin takunkuman da ta ƙaƙaba wa ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Guinea.

Ƙungiyar ta ɗauki matakin ne a wani taron shugabannin ƙasashen ƙungiyar da aka gudanar a Abuja babban birnin Najeriya.

Ƙungiyar ta ce a yanzu za ta iya gayyatar ƙasashen huɗu zuwa tarukanta da suka shafi tsaro da zaman lafiya.

Ecowas ta ce ɗage takunkuman – wanda zai fara aiki nan take – ta yi shi ne bisa dalilai na jin kai.

Huka kuma ƙungiyar ta jaddada kiranta na sakin hamɓararreb shugaban Nijar Mohamed Bazaoum da sojojin ƙasar ke ci gaba da yi wa ɗaurin talala.

Ecowas ta kaƙaba wa ƙasashe takunkuman ne bayan da sojoji suka kifar da gwamnatocin fara hula a ƙasashen.

Daga cikin takunkuman da ƙungiyar ta ƙaƙaba wa ƙasashen sun haɗa da rufe iyakokin ƙasashen da na ƙungiyar da kuma yanke wutar lantarki a Nijar da sauran takunkuman karya tattalin arziki.

Read Also:

  • ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa
  • Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027
  • Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar Neja

A makonnin baya-bayan ne ƙasashen Nijar, MAli da Burkina Faso suka ayyana ficewa daga ƙungiyar bayan da suka zargi ƙungiyar Ecowas da ƙaƙaba musu takunkuman karya tattalin arziki.

Ecowas ta riƙa fuskantar matsin lamba daga ƙungiyoyi da ɗaiɗaikun mutane kan ta ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Ko a makon da ya gabata ma tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya Janar Yakubu Gowan wanda shi ne mutum ɗaya tilo da ya rage cikin shugabanin da suka kafa ƙungiyar, ya yi kira ga shugabanninta da su ɗage wa ƙasashen takunkuman.

Nijar ta samu kanta cikin takunkuman Ecowas bayan da sojojin kasar suka kifar da gwamnatin farar hula da Mohamed Bazoum cikin watan Yulin shekarar da ta gabata.

Dama dai masu sharhi sun daɗe suna ta kiraye-kiraye ga shugabannin ƙungiyar su yi kaffa-kaffa, su mai da hankali wajen lalamar ‘ya’yan kungiyar idan ba haka ba garin gyaran gira a rasa ido.

Duk da cewa tun da farko shugabannin kungiyar Ecowas ɗin sun cije a kan matsayinsu na dakatar da kasashen da suka bijire wa demokuradiyyar tare da sanya musu takunkumi,

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Previous articleGwamnatin Nijeriya ta sake bude kantin Sahad na Abuja
Next article‘Yan bindiga sun yi awon gaba da dalibai sama da 100 a jihar Kaduna
Burkina Faso, Ecowas, Guinea, Mali, Nijar

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa

Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027

Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar Neja

Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno

Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Amurka ta fara kai harin soji Arewacin Nijeriya

Sojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a Borno

Gwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwa

ADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar haraji

Gwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen waje

Tinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRA

ICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRA

Recent Posts

  • ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa
  • Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027
  • Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar Neja
  • Sojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a Borno
  • Nan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -Tinubu

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1666 days 19 hours 20 minutes 58 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1648 days 21 hours 2 minutes 24 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsaKu daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar NejaSojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a BornoNan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -TinubuAmurka ta fara kai harin soji Arewacin NijeriyaSojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a BornoGwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwaADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar harajiGwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen wajeTinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRAICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRAZa mu ci gaba da kamen masu bakin gilashin mota - Yan sandaMajalisa ta amince da naɗin sabbin jakadun da Tinubu ya gabatarShugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna - Kotun Ƙoli
X whatsapp